Tattaunawa kan rikicin Bangui ya cije
January 10, 2013Tattaunawa kan rikicin Jamhuriyar Afirka ta tsakiya ya tashi ba tareda tsinan komai ba, inda aka tashi ba tare da yan tawaye da gwamnati sun amince da tsagaita wuta ba. Tattaunawar farko ta ƙare a jiya Laraba, ba tare da ko wane bangare ya nuna alamar ajeyi makami ba, a fadan da aka yi wata guda ana yi. Su dai yan tawayen ƙungiyar Seleka sun buƙaci shugaba Francois Bozize da ya yi murabus. Dama dai ƙungiyar ƙasashen yakin tsakiyar Afirka tare tallafin MDD da ƙasar Amirka suka shirya tattaunawar. Da farko dai an yi zaton farfado da yarjejeniyar da aka cimma a shekara ta 2007, amma yan tawaye suka ce wacan tattaunawa shugaba Bozize ya saɓa mata. Za dai aci gaba da ƙoƙarin shawo kan ɓangororin biyu a wata sabuwar tattauanwar a yau Alhamis.
Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Umaru Aliyu