1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsananin boren neman murabus na Zuma

April 7, 2017

Masu zanga-zanga sun mamaye biranen Afirka ta Kudu inda suke kiraye-kirayen saukar shugaban kasar daga mulki.

https://p.dw.com/p/2asiK
Südafrika Proteste gegen Präsident Zuma
Hoto: Reuters/M. Hutchings

Sama da mutane dubu 30 ne suka yi zanga-zanga a kasar Afirka ta Kudu a wannan Juma'a, inda suke kiran shugaba Jacob Zuma na kasar da ya yi murabus.

Dubban masu boren da suka bazu a manyan garuruwan kasar, na kiran saukar shugaba Zuman ne bayan garanbawul da shugaban ya yi a majalisar ministocin kasar. Bayanai sun ce 'yan sandan kasar na amfani da albarusan roba da kuma barkonon tsohuwa kan wasu 'yan jam'iyar ANC a birnin Johannesburg, wadanda ke kokarin nuna fushi kan 'yan adawar kasar, ta hanyar afka masu.

Matakin sallamar ministan kudin kasar cikin garambawul da shugaba Zuma ya yi a ranar Alhamis na makon jiya, ya tayar da jijiyoyin wuya a kasar, ciki kuwa har da 'ya'yan jam'iyyar ANC mai mulki tun cikin shekara ta 1994 bayan mulkin farar fatan kasar.