1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsokacin Ostareliya kan sakamakon binciken jirgin MH17

Salissou BoukariOctober 14, 2015

Bayan sakamakon biciken da aka bayar na ranar Talata kan faduwar jirgin kanfanin kasar Malesiya a gabashin Ukraine, hukumomin kasar Ostreliya sun sanar da matsayinsu.

https://p.dw.com/p/1GnYw
Tony Abbott Firaministan Ostareliya
Tony Abbott Firaministan OstareliyaHoto: picture-alliance/dpa

A wannan Laraba ce dai hukumomin kasar ta Ostreliya suka ce ba za su amince da duk wani ban tsoro ba, a daidai lokacin da suke neman hakkoki mutanansu daga shari'a. Daga cikin Fasinjojin jirgin 298 da suka rasu yayin wannan hadari dai, 38 dukanninsu 'yan kasar ta Ostreliya ne ko kuma suna zama a kasar. Duk dai da cewa sakamakon bai nuna wanda ke da alhakin kakkabo jirgin ba, amma kuma hukumomin kasar Ukraine da ma kasashen yamma, na zargin 'yan tawayan gabashin kasar ta Ukraine masu goyon bayan Rasha da aikata wannan laifi, zargin da tuni Rasha ta yi watsi da shi, inda ta dora alhakin hakan ga hukumomin Ukraine.