1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tunisiya ta katse hanzarin 'yan ta'adda

October 20, 2014

Humomin kasar Tunisiya sun bayyana dakile hare-hare masu nasaba da ta'addanci

https://p.dw.com/p/1DYue
Hoto: Imago

Mahukuntan kasar Tunisiya sun bayyana dakile hare-haren tsageru kan jami'an diplomasiya da harkokin tattalin arzikin kasar, a makonnin da suka gabata.

A wannan Litinin ministan harkokin cikin gida Lotfi Ben Jeddou ya ce 'yan ta'addan sun yi yunkurin kai hare-haren bama-bamai da motoci, kan jakadun kasashen ketere, da wasu kamfanoni amma jami'an tsaro suka dakile, sai dai jami'in bai yi karin haske ba. Tuni ma'aikatar cikin gidan ta ce za a jibge jami'an tsaro kimanin 46,000, domin tabbatar da doka da oda, yayin zaben mako mai zuwa a kasar ta Tunisiya da ke yankin arewacin Afirka.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Pinado Abdu Waba