1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Tsare wasu lauyoyi a Turkiya

Lateefa Mustapha Ja'afarMarch 16, 2016

Kungiyar lauyoyi a Turkiya ta sanar da cewa jami'an 'yan sanda sun tsare wasu lauyoyi guda takwas a ci gaba da kokarin murkushe magoya bayan Kurdawa 'yan fafutuka a kasar.

https://p.dw.com/p/1IEAA
Shugaban kasar Turkiya Racep Tayyip Erdogan
Shugaban kasar Turkiya Racep Tayyip ErdoganHoto: Getty Images/AFP/A.Altan

Wannan dai na zuwa ne jim kadan bayan da Shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiyan ya sanar da cewa zai fadada ma'anar ta'addanci a kasar, inda zai hadar da malaman makarantu da jami'oi da kuma 'yan jarida da ma 'yan adawar kasar. Tsare wadannan lauyoyi dai ya biyo bayan cafke wasu malaman makaranta guda uku a Turkiya bisa zarginsu da farfagandar ayyukan ta'addanci da aka yi a jiya Talata. Su dai malaman an kama su ne bayan da suka sanya hannu kan wani koke da ke yin tir da matakan da sojojin kasar ke dauka a kan jam'iyyar Kurdawa ta PKK a kasar.