1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Turkiyya na juyayin juyin mulki na 2016

Mouhamadou Awal Balarabe
July 15, 2017

Hukumomin Turkiyya na bikin tunawa da yunkurin juyin mulki da ya ci tura bayan da ya salwantar da rayukan mutane 249 a 2016. Sai dai suna ci gaba da korar ma'aikata da ake zargi da hannu a yunkurin daga bakin aiki.

https://p.dw.com/p/2gaz5
Türkei Putschversuch
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Suna

Kasar Turkiyya na juyayin yunkurin juyin mulki da aka gudanar a ranar 15 ga watan Yulin 2016, wanda shugaban Recep Tayyip Erdogan ya zargi shahararren malamin Musuluncin nan Fettullah Gülen da kitsawa. Majalisar dokokin kasar na zama na musamman da nufin tunawa da mutane 249 suka rasa rayukansu a wannan juyin mulki da ya ci tura.

Fadar mulki ta Ankara ta kama magoya bayan Gülen dubu 50, yayin da ta kori ma'aikata fiye da dubu 100 da ke da alaka da shi daga bakin aiki. Ko da a ranar Jumma'a ma sai da gwamnatin ta Turkiyya ta sallami ma'aikatan gwamnati fiye da dubu bakwai bisa zargin marar hannun a juyin na mulki da aka murkushe.

Abokan adawar Shugaba Erdogan sun zarge shi da neman fakewa da yunkurin juyin mulkin, wajen aiwatar da salon mulkin kama karya don dawwama a kan karagar mulki. Sai dai magoya bayansa sun danganta yunkurin da hanyar tabbatar da dimukaradiyya a Turkiyya.