1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

UNICEF: Harin bama-bamai da yara na karuwa

Salissou Boukari
April 12, 2017

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya ya fidda wani rahoto da ke cewar yawan yaran da 'yan Boko Haram ke dauka domin aiwatar da kai hare-haren kunar bakin wake na karuwa sosai.

https://p.dw.com/p/2b5yD
Kongo Brazzaville Unicef Fehlernährung
Hoto: DW/A.Severin

Asusun kula da yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya yi gargadi da kakkausar murya kan yadda kungiyar Boko Haram ke kara amfani da yara musamman mata domin kai hare-haren bama-bamai na kunar bakin wake a shiyar Arewa maso Gabashin Najeriya. 

Asusun na UNICEF ya bayyana wannan gargadi ne a wani sabon rahoto na karshen watanni uku na farkon shekara ta 2017, UNICEF ya ce an kai harin kunar-bakin-wake kimanin 77 a Najeriya da kasashen Chadi, da Kamaru da ke makobtaka da Najeriya wadanda suka fi fama da hare-haren kungiyar Boko Haram a yankin gabar Tafkin Chadi.

Nigeria Schule Initiative Unicef Dalori Camp
Hoto: picture-alliance/dpa/Unicef/Esiebo

Tun daga shekara ta 2014 zuwa yanzu rahoton ya nuna cewa an yi amfani da kanan yara 117 wajen kai hare-haren kunar-bakin-wake a wuraren taruwar jama'a kamar kasuwanni da wuraren ibada a kasashen Najeriya da Chadi da Nijar da kuma Kamaru.

A shekara ta 2014 da rahotanni suka nuna an samu hudu da aka fara amfani da su wajen kai harin kunar bakin wake inda aka samu 56 a cikin 2015, da kuma 30 a shekara ta 2016.

Somalia Flüchtlingslager in Doolow
Hoto: picture-alliance/Photoshot

Kimanin kananan yara 27 ne wannan rahoton ya nuna cewa Kungiyar ta Boko Haram tayi amfani da su wajen kai hare-haren kunar bakin wake daga watan Janairu zuwa watan Maris na wannan shekara abin da ya ke nuna cewa ana samun karuwar amfanin da yaran wajen kai hare-hare.

Sai dai a wata tattaunawa da aka yi da kwamishinar kula da harkokin mata ta jihar Borno Hon Fanta Baba Shehu ta ce mataki daya ne za a bi a magance wannan matsalar shi ne na ilimantar da mata da yara. Babbar jami'ar Asusun UNICEF mai kula da Nahiyar Afirka ta Yamma da kuma Afirka ta Tsakiya Marie-Pierre ta bayyana a cikin wannan rahoton cewa wannan shi ne cin zarafin yara mafi muni da aka taba samu a rikice-rikice a fadin duniya.