1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

von der Leyen za ta yi murabus

Abdul-raheem Hassan
July 16, 2019

Ministar tsaron Kasar Jamus Ursula von der Leyen da ke zama cikin 'yan takarar shugabancin kungiyar tarayyar Turai, ta ce za ta mara wa kudurin karawa Birtaniya wa'adin cimma yarjejeniyar ficewa daga kungiyar EU.

https://p.dw.com/p/3M86Q
Ursula Von der Leyen
Hoto: picture-alliance/AA/D. Aydemir

Wannan dai na cikin jerin alkawuran da ministar ta shimfide gaban 'yan majalisun kungiyar tarayyar Turai a wani mataki na nuna alamun sassaucin shugabacin domin samun goyon baya a zaben shugabancin kungiyar. Sai dai ministar tsaron ta Jamaus ta tabbatar da yin murabus daga mukaminta gabannin fara zaben ko za ta yi nasarar zama sabuwar shugabar kungiyar ta EU ko akasin haka.