1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Wanzuwar rikici a garin Kidal na kasar Mali

November 30, 2013

'Yan tawayen Mali sun bayyana sake daukar makamai domin yakar gwamnati

https://p.dw.com/p/1AQzJ
FILE - In this Friday, July 26, 2013 file photo, rebels from the National Movement for the Liberation of the Azawad (NMLA) stand guard outside the former governor's office, in Kidal, Mali. Malian soldiers and ethnic Tuareg separatist rebels clashed again in the northern desert town of Kidal early Monday, Sept. 30, 2013, a day after trading gunfire downtown in a battle that has raised fears about whether an unraveling peace accord could lead to protracted fighting in the region. (AP Photo/Rebecca Blackwell, File)
Hoto: picture alliance/AP Photo

'Yan awaren kasar Mali sun kawo karshen yarjejeniyar tsagaita bude ta watanni biyar da suka kulla tare da gwamnatin kasar, kana sun sake daukar makamansu, bayan wasu rigingimun da aka samu a garin Kidal da ke yankin arewacin kasar. Ayyana wannan kudirin, ya zo ne yini daya kachal bayan da dakarun gwamnatin Mali suka yi fito na fito da masu zanga zangar da suka hana fira ministan kasar shiga garin Kidal yayin wata ziyarar da ya shirya yi a garin, wanda ke zaman sansani ne ga 'yan tawayen. Kazalika, matsalar ta biyo bayan zagaye na farko ne na zaben majalisar dokokin kasar da ya gudana a ranar Lahadin da ta gabata. Yawan wadanda suka jefa kuri'a a lokacin zaben dai, ba su kai kaso 40 cikin 100 na wadanda suka cancanci jefa kuri'a ba, kuma a watan gobe - idan Allah ya kaimu al'ummar kasar Mali za ta je rumfunan zabe domin gudanar da zagaye na biyu na zabukan majalisar dokokin.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Usman Shehu Usman