1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Warware saɓani tsakanin Hamas da Fatah

November 19, 2012

Musayar harbe-harbe a tsakanin Isra'ila da zirin Gaza ta tilastawa Hamas da Fatah dunƙulewa wuri guda.

https://p.dw.com/p/16leN
Palestinians run for cover as tear gas canisters are fired by Israeli soldiers during clashes in the West Bank town of Nablus, on November 18, 2012, as Palestinian across the territories protest against Israel's military action on the Gaza Strip. Israel's Foreign Minister Avigdor Lieberman said that Israel would not negotiate a truce with Gaza Strip's Hamas rulers as long as rocket fire continues from the Palestinian enclave. AFP PHOTO / JAAFAR ASHTIYEH (Photo credit should read JAAFAR ASHTIYEH/AFP/Getty Images)
Hoto: JAAFAR ASHTIYEH/AFP/Getty Images

A yayin da Isra'ila ke ci gaba da ƙaddamar da hare-hare ta jiragen sama akan zirin Gaza na Falasɗinu, kuma take fuskantar martanin rokoki, ƙungiyoyin Hamas da Fatah na Falasɗinawa, waɗanda ba sa ga maciji da juna sun bayyana dunƙulewa wuri guda domin nuna goyon bayan su ga zirin na Gaza.

Wani jigo a ƙungiyar Fatah Jibril Rajoub, ya shaidawa wani taron masu zanga-zangar da yawan su yakai mutane dubu ɗaya a yankin gaɓar tekun Jordan, da ke zama hedikwatar Falasɗinu cewar, daga wannan lokacin, yana tabbatarwa da duniya cewar sun kawo ƙarshen taƙaddamar da ke tsakanin su. Daga ciki waɗanda suka halarci taron na yankin gaɓar tekun Jordan - harda shugabannin ƙungiyar Hamas a yankin da kuma na ƙungiyar Islamic Jihad.

Wannan ci gaban dai na zuwa ne a dai dai lokacin da Isra'ila ta shiga yini na shidda a jere wajen farmakin da take ƙaddamarwa a Gaza, wanda ke ƙarƙashin ikon ƙungiyar Hamas, kana 'yan ƙungiyar ta Hamas kuwa ke jefa rokoki a cikin Isara'ila.

A halin da ake ciki kuma, shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel, ta bayyana yiwuwar tsagaita buɗe wuta a rikicin na zirin Gaza, yayin da ministan kula da harkokin wajen na Jamus Guido Westerwelle ya kama hanyarsa ta zuwa birnin Tel Aviv na Isra'ila. A cewar Steffen Seibert, kakakin shugabar gwamnatin Jamus, Merkel na fargabar yiwuwar rikicin na Gaza, ya tsananta rigingimun da dama yankin na Gabas Ta Tsakiya ke fama da shi.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mohammad Nasir Awal