1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

WHO: Mun gamsu da rigakafin Ebola

Zulaiha Abubakar
May 29, 2018

Mataimakin Darakta mai kula da agajin gaggawa na Hukumar Lafiya ta Duniya Dakta Peter Salama ya bayyana gamsuwarsa tare da kyakykyawan fatan samun nasarar rigakafin cutar Ebola a Jamhuriyar Demokradiyyar Kwango.

https://p.dw.com/p/2yX2M
DR Kongo Ebola Ausbruch
Hoto: Reuters/K. Katombe

Dakta Salama ya bayyana hakan ne yayin da hukumar ta samu nasarar yi wa kashi chasa'in na mutanen da suka yi ta'ammali da wadanda suka kamu da cutar Ebola a Kwango allurar ta rigakafi. Daga nan sai ya kara da cewar Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) na duba yiwuwar fara amfani da wasu magungunan gwaji guda biyar na cutar ta Ebola a fadin kasar ta Kwango.