1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaƙi da cutar masassarar tsuntsaye a ƙasar Jamus

March 3, 2006
https://p.dw.com/p/Bv6D

Ministan ayyukan gona na ƙasar Jamus Horst Seehofer yace maáikatar sa za ta dauki wasu kwararan matakai da nufin kare yaɗuwar cutar murar tsuntsaye a ƙasar. Ministan yace a halin da ake ciki, hukumomi na duba yiwuwar taƙaita kai komon jamaá a gonakin kiwon kaji inda aka sami ɓullar cutar a Jamus. A waje guda kuma, jamián kiwon lafiya sun tabbatar da ƙwayar cutar H5N1 a jikin wata mage da ta mutu a tsibirin Rügen dake arewacin Jamus. A Ɓangare guda, Jamián kiwon lafiyar dabbobi na ƙungiyar tarayyar turai sun shawarwaci masu dabbobi na cikin gida, su killace dabbobin na su waɗanda suka hada da mage da karnuka musamman a yankunan da aka sami bullar cutar ta masassarar tsuntsaye.