1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaki da masu tada tarzoma a Masar

September 9, 2013

A yayin da Masar ke kai hari don kawar da masu tada tarzoma a Sina'i , wata kungiya a yankin ta dauki alhakin neman kissan wani jami'i a kasar.

https://p.dw.com/p/19dyU
Bildnummer: 59670080 Datum: 21.05.2013 Copyright: imago/Xinhua (130520) -- SINAI, May 20, 2013 (Xinhua) -- Egyptian Army vehicles with tanks head to al-Arish in northern Sinai, near the Rafah border crossing between Egypt and the Gaza strip, Egypt, May 20, 2013. On Thursday, a group of militants, believed to be members of the hardline Jihadist group, abducted seven Egyptian military recruits from the police and the military in North Sinai s Green Valley, some 20 km away from Arish. The Egyptian presidency said on Monday that all options are open in dealing with the kidnappers of the Sinai soldiers and securing their release. (Xinhua/STR) EGYPT-SINAI-SECURITY-KIDNAP PUBLICATIONxNOTxINxCHN Gesellschaft Militär premiumd x0x xsk 2013 quer 59670080 Date 21 05 2013 Copyright Imago XINHUA Sinai May 20 2013 XINHUA Egyptian Army VEHICLES With Tanks Head to Al Arish in Northern Sinai Near The Rafah Border Crossing between Egypt and The Gaza Strip Egypt May 20 2013 ON Thursday a Group of militant believed to Be Members of The hard line Group Abducted Seven Egyptian Military recruits from The Police and The Military in North Sinai S Green Valley Some 20 km Away from Arish The Egyptian Presidency Said ON Monday Thatcher All Options are Open in Dealing With The Kidnappers of The Sinai Soldiers and Securing their Release XINHUA Str Egypt Sinai Security PUBLICATIONxNOTxINxCHN Society Military premiumd x0x xSK 2013 horizontal
Hoto: imago stock&people

Wata kungiyar mayakan sa kai dake arewacin zirin Sina'i na Masar, ta yi ikirarin cewar, ita ce ta kai hari, amma wanda bai yi nasara ba, da nufin kissan ministan kula da harkokin cikin gidan Masar. Dama dai wani bam da mayakan sa kai suka so tayarwa da nufin kissan Mohammed Ibrahim, ya janyo mutuwar wasu fararen hula dake kusa da wurin da suka tada bam din, game da haddasa rauni ga fiye da mutane 20.

A halin da ake ciki kuma, wasu jiragen yaki - masu saukar ungulu sun yi ta ruwan bama-bamai a wuraren da jami'an tsaron na Masar suka ce maboyar masu tada tarzoma ne a zirin na Sina'i - yini na biyu kenan - a jere a wannan Lahadin (08.09.13). Jami'an tsaron sun kara da cewar, manufar kaddamar da hare haren, ita ce fatattakar kungiyoyin sa kai, wadanda ke da alaka da kungiyar alQa'ida daga kauyuka daban daban da ke kan iyakar, inda suka ce mayakan suna da runbunan makamai, kuma suke neman samun gindin zama.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mouhamadou Awal Balarabe