1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yaki na kara yin muni a Raqqa

Abdourahamane Hassane
August 24, 2017

Kungiyar kare hakin bil Adama ta Amnesty International ta ba da rahoton cewar dubban fararan hula sun makale a garin Raqqa na Siriya cibiyar mayakan Kungiyar IS

https://p.dw.com/p/2ijTc
Syrien Kämpfe um Rakka
Hoto: Reuters/Z. Bensemra

Majalisar Dinkin Diuniya ta ce akwai mutane kamar dubu 25 a birnin na Raqqa yayin da wasu dubbai suka yi kasada suka arce duk da ruwan wutar da ake yi. Tun lokacin da dakarun FDS suka fara kai farmaki a kan Kungiyar ta IS a cikin watan Yuni da ya gabata, sun kwaci kusan kishi 60 cikin dari na yankunan da kungiyar take da iko da su tun a shekar ta 2014 a Siriya.