1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yamen: Yarjejeniyar tsagaita wuta ta fara aiki

Abdoulaye Mamane Amadou
April 2, 2022

Bayan shafe tsawon shekaru ana gwabza yaki a Yamen 'yan tawaye sun cimma yarjejeniyar tsagaita buta wuta da kawancen sojan da kasar Saudiyya ke jagoranta.

https://p.dw.com/p/49O0T
Huthi-Rebellen im Jemen
Hoto: Hani Mohammed/dpa/AP/picture alliance

Yarjejeniyar da aka cimma karkashin jagorancin Majalisar Dinkin Duniya za ta shafe tsawon watanni biyu ne a kasar da yaki ya daidaita, kana kuma tuni ta soma aiki wannan Asabar daya ga watan Ramadana.

Bangarorin biyu da suka aminta da tsagaita buda wuta, sun kuma yi na'am da zirga-zirgar jirage daga wasu yankuna zuwa babban birnin kasar Yamen Sanaa, baya ga bude mashigar ruwa ta Hodeida da ke yammacin kasar ga tankokin dakon danyen mai, a cewar manzo na musamman na MDD da ya shiga tsakani Hans Grundberg.