1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan adawa sun lashe zaben Cape Verde

Suleiman BabayoMarch 21, 2016

'Yan adawa sun lashe zaben majalisar dokokin tsibirin Cape Verde karo na farko cikin shekaru 15.

https://p.dw.com/p/1IH5Y
Kapverdische Inseln Unterstützer der MpD
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Cruz

'Yan adawa a tsibirin Cape Verde sun lashe zaben majalisar dokoki a zaben da ya gudana wannan Lahadi da ta gabata. Babbar jam'iyyar adawa ta Movement for Democracy ta sake dawowa kan madafun iko bayan adawa na tsawon shekaru 15. Ita kuma jam'iyya mai mulki ta PAICV ta samu kashi 37 cikin 100.

Portugal ta yi wa tsibirin na Cape Verde da ke yammacin Afirka mulkin mallaka kuma yana makwabtaka da kasar Senegal, tsibirin ya kauce wa duk rikice-rikicen siyasa da suka ritsa da yankin na yammacin Afirka a shekarun da suka gabata. Kuma wani lokaci cikin wannan shekara za a gudanar da zaben shugaban kasa na kasar ta Cape Verde.