1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan adawa sun yi gangami a Kenya

Abdourahamane Hassane
October 6, 2017

'Yan sanda a garin Kisumu da ke a yammancin Kenya sun yi amfani da kulake da barkon tsohuwa wajen tarwatsa kimanin mutane dubu uku a sa'ilin wata zanga-zanga.

https://p.dw.com/p/2lOIY
Kenia Präsidentschaftswahl Proteste in Nairobi
Hoto: Reuters/T. Mukoya

A biranen Nairobi da Mombasa ma an gudanar da gangamin, sai da masu aiko da rahotanni sun ce jama'a da dama ba su fito ba. Bayan soke zaben kasar na Kenya da kotun ta yi a cikin watan Augusta da ya gabata 'yan adawar kasar sun kaddamar da wani kampe na nuna adawa da hukumar zaben wacce za ta shirya sabbin zabubukan da za a gudanar a ranar 26 ga wanan wata na Oktoba saboda abin da suka kira rashin adalcin manbobin hukumar.