1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan adawar Siriya za su shiga tattaunawa

Abdul-raheem Hassan
November 24, 2017

Gamayyar kungiyoyin 'yan adawa a Siriya sun amince da shiga tattaunawar zaman lafiya karkashin jagorancin MDD a Geneva. Tattaunawar da ake fata zai kawo karshen yakin basasa a kasar.

https://p.dw.com/p/2oAfT
Riad Treffen Syrische Opposition Mistura
Hoto: Getty Images/AFP/F. Nureldine

Wata sanarwa da kungiyoyin suka fitar na cewa za su aike da wakilai 50, da za su halarci taron Majalisar Dinkin Duniya kan zaman lafiya da zai gudana a birnin Geneva.

Matakin kungiyoyin ya zo ne yayin da suke ganawa a birnin Riyadh na kasar Saudiyya, da nufin cimma matsaya gabannin ganawa da shugaban kasar Siriya Bashar al-Assad a ranar 28 ga watan Nuwamba.

Cimma shawo kan kungiyoyin Siriyar ya samu nasara ne a kokarin masu shiga tsakanin na kasa da kasa, da ke kokarin kwantar da wutar rikici tsakanin 'yan adawa da bangaren gwamnati.

A baya dai MDD ta sha shirya tattaunawa da bangarorin biyu amma yana rugujewa. Yakin basasa a Siriya ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula sama da dubu 330,000, tare da tilasawa miliyoyin 'yan kasar tserewa matsugunansu.