1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan bindiga sun bude wa wani otel wuta a Cote d'Ivoire

Kamaluddeen SaniMarch 13, 2016

Wasu 'yan bindiga dauke da manyan makamai sun budewa wani otel wuta da ke zama matattarar masu shakatawar 'yan kasashen waje a kasar Cote d'Ivoire.

https://p.dw.com/p/1ICWN
Elfenbeinküste Anschlag Grand Bassam in Abidjan
Hoto: Reuters/J. Penney

Wadanda suka gane wa idanuwansu sun shaida wa kamfanin dillancin labaran AFP cewar 'yan bindigar wadanda suke sanye da kallaye a fuskokinsu, sun bude wa katafaren otel din shakatawar da ke shake da mutane a cikinsa wuta.

Kawowa yanzu dai hukumomin birnin Abidjan na kasar ba su bayyana ko mutane nawa ne suka mutu da kuma kasashen da suka fito ba.

Hare-hare a kan manyan otel-otel dai na cigaba da zama ruwan dare a kasashen Mali da Burkina Faso, a inda a 'yan kwanankin baya sai da wasu 'yan bindigar suka budewa wasu a kasashen wuta tare da hallaka da dama da ke yawan shakatawa da gidajen otel din.

Tuni hukumomin tsaron Cote d'Ivoire suka dukufa domin gano wadanda suka kai harin.