'Yan gudun hijira na Mali a Moritaniya sun yi zanga zanga.
February 5, 2013Gomai na yan gudun hijirar' na Mali da ke a Moritaniya, sun gudanar da yamutsi a cikin sansanin yan gudun hijira na Mberré da ke a yankin kudu maso gabashi Moritaniya kan iyaka da Malin.Masu aiko da rahotanin sun ce yan gudun hijirar, sun cire shingaye da aka dasa na wayoyi a wurraran da aka girke kayan abincin da a ke raraba masu.
Dangane da yadda suka yi Allah wadai da tsarin raraba abinci wanda sai an ja dogon layi.Wani daga cikin yan gudun hijirar ya ce wata mata ta haifu a cikin layin wajan jiran abinci yayin da wata matar ta mutu.MDD ta ce a kwai yan gudun hijira kusan dubu 18 waɗanda suka samu mafuka a cikin ƙasashe maƙofta na yammanci Afirka; galibi a Moritaniya da Burkina faso tun lokacin da sojojin Faransa suka kutsa kai a yankin arewacin Malin.
Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Umaru Aliyu