1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan jarida mata na fuskantar barazana

Abdourahamane Hassane BAS
March 5, 2018

Kungiyar 'yan jaridu ta kasa da kasa Reporters Without Borders (RSF) ta ce 'yan jaridu mata na fuskantar barazanar kisa da hukuba da kuma dauri a gidajen kurkuku a cikin wasu kasashen duniya.

https://p.dw.com/p/2tiZ7
Türkei Demonstranten unterstützen Pro-kurdische Zeitung Ozgur Gundem
Hoto: Getty Images/AFP/O. Kose

A cikin wani rahoton da ta bayyana daf da lokacin da ake shirin gudanar da bikin ranar mata ta duniya ran takwas ga watan Maris. Kungiyar ta RSF ta ce tsakanin shekara ta 2016 da 2017 an kiesta kamar mata 60 a cikin kasashe 20 wadanda suka samu kansu cikin irin wannan hali saboda aikin da suke yi na bincike kan halin rayuwar mata. Kassahen China da Masar da Turkiyya na daga cikin kasashen da matan 'yan jarida ke fuskantar galazawa.