1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan Kwango na ban kwana da Tshisekedi

Yusuf Bala Nayaya
May 31, 2019

Dubban 'yan kasar Kwango na zuwa filin wasa na babban birnin kasar don yin ban kwana da gawar tsohon jagoran adawa Etienne Tshisekedi.

https://p.dw.com/p/3JZCF
Ankunft der sterblichen Überreste von Etienne Tshisekedi, dem Vater des Präsidenten des Kongo, Felix Tshisekedi, in Kinshasa
Hoto: Presidence RDC

Tshisekedi dan shekaru 84 ya rasu a Beljiyam shekaru biyu da suka gabata amma mahukunta a wancan lokaci suka hana a dawo da gawarsa saboda fargabar kada hakan ya tada rikici a kasar. Sai dai an samu sauyi bayan da dan Tshisekedi ya yi nasarar zama shugaban kasa a zaben da aka yi a watan Janairu.

Tsohon shugaban kasar ta Kwango dai Joseph Kabila ya sauka daga kujerarsa bayan shekaru 18 yana kan karagar mulki. Bayan nasarar dan na Tshisekedi ne dai wato Felix Tshisekedi ya sha alwashi na dawo da gawar mahaifinsa don a binne ta a kasar ta Kwango.