1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan sanda na tsare da wasu 'yan jarida a Nijar

January 26, 2014

Gwamnatin na zargin 'yan jaridar da yunƙurin kawo fitina a cikin ƙasar da kuma wasu 'yan siyasa.

https://p.dw.com/p/1AxW4
Niger Präsident Mahamadou Issoufou
Hoto: Seyllou/AFP/Getty Images

Haɗin gwiwar ƙungiyoyin 'yan jaridu masu zaman kansu, sun bayyana wata sanarwa domin yin Allah wadai da matakin da gwamnatin ta ɗauka na kama wasu 'yan jaridun.

'Yan jaridun, waɗanda suka haɗa da Soumana Idrissa Maiga,Editan wata jarida mai zaman kanta, ta Enquetteur,da Abdullahi Maman, ɗan jaridan wani gidan talbijan mai zaman kansa Bonferey, kuma wakilin Muryar Amirka a Nijar. An kama su ne a kan zargin da gwamnatin ta ke yi musu na wallafa wasu bayanai da kuma yin muhawara da suka ce lamarin na iya kawo tashin hankali.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Saleh Umar Saleh