1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan Sudan hudu sun mutu a zanga-zanga

June 9, 2019

Rayuka sun sake salwanta a Sudan yayin da jami'an tsaro suka yi tsayuwar ganin bayan masu zanga-zangar adawa da manufofin mulkin soji. Masu fafutukar samar da sauyi ne suka yi kira da a gudanar da yajin aikin gama gari.

https://p.dw.com/p/3K6ta
Sudan Khartum - Unruhen
Hoto: Getty Images/AFP

Rahotannin da ke fitowa daga Sudan na cewa jami'an tsaron kasar sun halaka akalla mutum hudu daga cikin masu zanga-zanga da yajin aikin gama gari a wannan Lahadi. Tun da fari dai  jami'an 'yan sanda sun yi amfani da borkonon tsohuwa wajen tarwatsa masu zanga- zanga da suka daddasa shingaye a kan titunan domin datse zirga- zirgar motoci.

Wani kwamitin likitoci da ke da alaka da masu boren ya tabbatar da mutuwar mutanen biyu a Khartoum, wasu biyun kuma a Omdurman. Kungiyoyin masu fafutukar samar da sauyi a Sudan sun lashi takobin ci gaba da zanga-zangar adawa da gwamnatin har sai an kafa gwamnatin farar hula da suke bukata.