1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan tawaye na gwabza fada a Siriya

Abdul-raheem Hassan
July 19, 2017

Bangarorin 'yan tawayen na gwabza kazamin fada a tsakanin junan su, kungiyoyin sa'aido a kasar sun ce gumurzun wutan ya yi sanadiyar mutuwar mutane 11 daga dukkanin banagarorin biyu da wasu fararen hula uku.

https://p.dw.com/p/2go7C
Syrien Al-Raqqa - Kurdische Kämpfer
Hoto: Reuters/G. Tomasevic

Barkewar rikici tsakanin kungiyoyin biyu na zuwane kwanaki kalilan bayan da wata kungiyar 'yan tawaye ta kaddamar da kafa tuta a yankin Idlib, an dai kwashe tsawon sa'anni 24 ana fafatawa tsakanin kungiyar jihadi ta Hayat Tahri al-Sham da kungiyar Ahrar al-Sham dake zama  kungiyar 'yan tawaye mai karfin iko a yankin Idlib dake arewa maso yammacin kasar.

Kungiyoyin kare hakkin bil'adama a Siriya sun ce wannan ba shi ne karon farko da 'yan tawayen ke gwabzawa da juna ba, tun bayan da suka karbe iko da Idlib. A yanzu dai yankin na Idlib na cikin yankunan da dakarun gwamnatin Bashar al-Assad ke fatan karbe iko da su daga hannun 'yan tawayen Siriya.