1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Gwamnati ta yi sulhu da 'yan tawaye

Abdoulaye Mamane Amadou
February 5, 2019

Gwamnatin Jamhuriyar Afirka ta tsakiya ta sanya hannu kan wata yarjejeniyar tsagaita wuta da kungiyoyin ‘yan tawayen kasar a Khartoum babban birnin  kasar Sudan

https://p.dw.com/p/3CkUD
Zentralafrikanische Republik UN Soldaten
Hoto: Reuters/B. Ratner

Tun bayan hambare gwamnatin tsohon shugaban Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya Francois Bozize daga mulki a shekarar 2013, kasar ke fama bulluwar kungiyoyin sa kai masu dauke da makamai, wadanda ke rike da kashi 80 cikin dari na fadin kasar.

Yarjejeniyar wacce ke karkashin jagorancin kungiyar Tarayyar Afirka ta AU, ta kai ga shawo kan kungiyoyin ‘yan tawaye 14 da ke gwaggwarmaya ya zuwa ga samun masalahar ne, kwanaki bayan an yi hannun riga kan batun raba mukamai da batun yafiya ga shugabannin kungiyoyin masu yakin sunkuru.