1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yunkurin hari ga mabiya addinin koptik a Masar

January 7, 2013

Mabiya addinin koptik a kasar Masar na yawan fuskantar barazana daga masu tsautsauran kishin islama.

https://p.dw.com/p/17FHt
Mabiya koptik na MasarHoto: Getty Images/AFP

Rundunar tsaro ta kasar Masar,ta bada sanarwar gano wata makerkeshiyar yunkurin kai hari a wata cocin mabiya addinin koptik a daidai lokacin da suke shugulgulan bukukuwan kristimati a wannan Litanin Da sahin subahin din safiyar yau ne,wani ayarin sojoji da ke sintirin a garin Rafah da ke kan iyaka da yankin zirin Gaza,suka cafke wasu mutane guda hudu dauke da nakiyoyi shake a cikin mota. Tuni kuma aka mika mutanen ga jami'an 'yan sanda da ke ci-gaba da yi musu bincike. Ana dai saran mutanen da suka fito daga yankin Zirin Gazan,masu tsautsauran kishin islama ne. Ko a shekarar bara,wani makamancin hakan ya faru,inda wasu mutanen da ba a gano ko su wane ba,suka tada bom a wani ginin mabiya addinin koptik,inda a kala mutane 3 suka rasa rayukansu.

Mawallafi: Issoufou Mamane

Edita: Mahamadou Awal Balarabe