1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci kulla yarjejeniya a Libiya

Abdoulaye Mamane Amadou
August 9, 2019

Majalisar Dinkin Duniya ta bukaci bangarorin da ke fada da juna a Libiya da su tsagaita wuta don bai wa jama'a damar samun sukunin gudanar da bukukuwan Sallah ba tare da fitina ba.

https://p.dw.com/p/3Nehb
Libyen Bürgerkrieg
Hoto: AFP

Majalisar Dinkin Duniya ta ce tana mai fatan samun cimma wata kwarya-kwaryar yarjejeniya daga bangarorin biyu da ke yaki da makamai a yau din nan, tare da fatan soma aiki da yarjejeniya tun daga gobe Asabar har  zuwa karshen bukukuwan na babbar sallah.Tun a cikin watan Aprilun wannan shekarar ne sojojin da ke biyayya ga madugun yaki Khalifa Haftar suka yunkuri aniyar kwace iko da birnin Tripoli a hannun gwamnatin hadin kan kasar mai samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya, rikicin.