1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Yunkurin zaman lafiya a Kongo

December 1, 2012

'Yan tawayen M23 sun fara janyewa daga garin Goma da suka kwace daga dakarun gwamnatin Kongo.

https://p.dw.com/p/16uDE
M23 rebels withdraw from the Masisi and Sake areas in the eastern Congo town of Sake, some 27 kms west of Goma, Friday Nov. 30, 2012. Rebels in Congo believed to be backed by Rwanda postponed their departure Friday from the key eastern city of Goma by 48 hours for “logistical reasons,” defying for a second time an ultimatum set by neighboring African countries and backed by Western diplomats. The delay raises the possibility that the M23 rebels don’t intend to leave the city they seized last week, giving credence to a United Nations Group of Experts report which argues that neighboring Rwanda is using the rebels as a proxy to annex territory in mineral-rich eastern Congo.(Foto:Jerome Delay/AP/dapd).
Hoto: AP

'Yan tawayen M23 da suka kwace iko da garin Goma na hamhuriyyar Doimokradiyyar Kongo tun a ranar 20 ga watan Nuwamban nan, sun fara janyewa daga garin suna yin wake-wake da wasa da makamai a wannan Asabar. Wannan matakin da suka dauka dai ya karfafa fatan kokarin samar da zaman lafiya da kuma tattaunawar kawo karshen rigingimun da yankin ya fada ciki a baya bayannan.

Kimanin mako guda kenan da shugaban Uganda, dake zama shugaban kungiyar kasashen yankin Great Lakes ya jagoranci wani shirin sulhu, wanda a lokacin ne kuma ya bukaci 'yan tawayen su janye daga birnin na Goma bayan da suka fatattaki sojojin gwamnatin jamhuriyyar Dimokradiyyar Kongo da ke samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya. A da dai 'yan tawayen sun sha alwashin kifar da gwamnatin shugaba Josef Kabila, wadda ke da hadikwata a birnin Kinshasa.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Yahouza Sadissou