1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Za a kai agaji ga mabukatan Siriya

Abdulraheem HassanJune 9, 2016

Gwamnatin kasar Siriya ta bada izini ga kungiyoyin da ke aikin agaji da su kai kayan abinci a wurare 19 da aka killace a cikin wannan watan da muke ciki.

https://p.dw.com/p/1J3z8
Syrien UN-Gesandt Staffan de Mistura bei Baschar al-Assad in Damaskus
Hoto: picture-alliance/dpa

Wakilin Majalisar Dinkin Duniya a Syrian Staffan De Mistura, ya nuna da cewa yana kyautata zaton motocin kai kayan za su isa wuraren da ake tsammani a cikin lokaci. Dubban 'yan kasar Siriya ne dai ke fama da tsananin yunwa, kuma basa samun agaji daga kungiyoyin bada tallafi, sakamkon yadda gwamnati da 'yan tawaye suka killace yankunan da suke iko da su, a matsayin neman mika wuya ga abon kan gaba.