Zaman ɗar-ɗar tsakanin Koriya ta Kudu da ta Arewa
April 1, 2013Shugaba Park Geun-Hye ta Koriya ta Kudu ta ce kasar ta ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen maida martani muddin Koriya ta Arewa ta kai mata hari.
Uwargida Park ta ambata hakan ne a wannan Litinin din bayan da ta gudanar da wani taron gaggawa da manyan jami'an sojin kasar da kuma ministan tsaron kasar Kim Kwan-Jin, biyo bayan shelar da Pyongyang ta yi cewar Koriyoyin biyu na ciki wani yanayi na yaki.
Wadannan kalamai na shugaba Park na zuwa ne daidai lokacin da 'yan majalisar dokokin Koriya ta Arewa wadda ake yi wa kallon 'yan amshin shata ta ke dab da gudanar da wani babban taronta na shekara-shekara wanda zai duba batutuwa da su ka shafi kasar da ma dai dangantaka tsakanainta da Koriya ta Kudu.
Tuni dai kasashen da ke yankin su ka fara yin kiraye-kiraye ga kasashen biyu da su kai zuciya nesa domin gudan fadawa yaki wanda a cewarsu ba zai amfana mu su da mai idanu ba.
Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Usman Shehu Usman