1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zaman lafiya ba zai samu ba ta hanyar gina matsugunai-Abbas

March 21, 2013

A wani taron manema labaru na hadin guiwa da suka yi da Barack Obama a Ramallah, Mahmud Abbas ya ce fadada matsugunan Yahudawa na kawo cikas ga shirin zaman lafiya.

https://p.dw.com/p/181ib
U.S. President Barack Obama and Palestinian President Mahmoud Abbas (R) shake hands at a news conference at the Muqata Presidential Compound in the West Bank City of Ramallah March 21, 2013. REUTERS/Larry Downing (WEST BANK - Tags: POLITICS)
Hoto: Reuters

Shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas ya fada wa shugaban Amirka Barack Obama da ya kai wata gajeriyar ziyara a Gabar Yamma ta Kogin Jordan cewa ba za a samu zaman lafiya da Isra'ila ta hanyar tashe tashen hankula, mamaya da gina matsugunan Yahudawa da kuma kin amincewa da 'yancin 'yan gudun hijira ba. Abbas ya fadi hakan ne a wani taron manema labarai na hadin guiwa da suka yi da shugaba Obama a birnin Ramallah. Kalaman dai na daga cikin jerin korafe korafe da Falasdinawa ke wa Isra'ila. Abbas ya jaddada bukatar kafa wata kasar Falasdinu a Gabar Yammacin Kogin Jordan, Gaza da kuma gabacin Birnin Kudus, yankunan da Isra'ila ta kwace a yakin shekarar 1967, wanda kuma tun a wancan lokaci kasar ta Yahudun Isra'ila ta yi ta gina dubban matsugunan Yahudawa 'yan share wuri zauna. Shi ma a nasa bangaren shugaba Obama ya yi tir da aikin gina unguwannin Yahudawan da Isra'ila ke ci-gaba da yi, abin da ya ce yana kawo cikas ga kokarin samar da zaman lafiya.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe