1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Sace daliban Zamfara ya janyo hana shawagin jiragen sama

Ramatu Garba Baba
March 4, 2021

A sakamakon yawaitar aiyukan 'yan bindiga ne gwamnatin tarayyar Najeriya ta dakatar da aikin hakar ma'adinai dama shawagin jiragen sama a sararin samaniyar jihar Zamfara da ke arewacin kasar.

https://p.dw.com/p/3qDU2
Weltspiegel 03.03.2021 | Nigeria Zamfara | Freilassung entführter Schulmädchen
Hoto: Afolabi Sotunde/REUTERS

A ci gaba da kokarin neman mafitar rashin tsaron da ke dada kamari a cikin tarrayar Najeriya, majalisar tsaron kasar ta dakatar da aiyukan hakar ma'adinai a jihar Zamfara, ko bayan haramta shawagi na jirage a cikin yankin. Tun bayan satar mata 'yan makarantar Sakandaren Jangebe da ke cikin jihar ta Zamfara, hankulan daukacin kasar ya karkata ya zuwa sabuwar sana'ar satar dalibai da ke dada samun farin jini a tsakanin 'yan ina da kisan.