1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar adawa da G5 Sahel a Bamako

Gazali Abdou Tasawa
May 23, 2019

A Mali, daruruwan mazauna Bamako sun shiga wani zaman dirshen a gaban sabuwar hedikwatar rundunar yaki da ta'addanci ta G5 Sahel domin nuna rashin amincewarsu da girka sabuwar hedikwatar rundunar a birnin.

https://p.dw.com/p/3Ivwr
Sahel Konflikt - Malische Armee
Hoto: Getty Images/AFP/D. Benoit

Bayan da suka gicce babbar hanyar da ke zuwa sabuwar hedikwatar rundunar ta G5 Sahel daga bisani masu zanga-zangar sun kuma kafa runfunan a gaban cibiyar inda suka shiga zaman dirshen wanda suka ce za su kwashe kwanaki biyu suna yi. 

Kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP ya ruwaito Mariam Keita wakiliyar kungiyar matan sojojin Mali, daya daga cikin masu zaman dirshen din na cewa ba sa kaunar ganin sojojin rundunar ta G5 Sahel a birnin na Bamako, su tattara su koma a yankin arewacin kasar ta Mali da ke zama filin daga, idan dai har da gaske suke cewa suna yaki ne da ta'addanci. 

An maido da hedikwatar rundunar ta G5 Sahel ne a birnin na Bamako ne bayan harin da 'yan ta'addan suka kai a cibiyarta ta farko da ke a birnin Sevare na tsakiyar kasar a ranar 29 ga watan Yunin bara.