1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zanga-zangar goyon bayan jami'an tsaro a Nijar

Salissou BoukariJuly 9, 2016

Daruruwan mutane ne suka yi zanga-zanga ta lumana a wannan Asabar din a Yamai babban birnin Jamhuriyar Nijar, da ma wasu manyan biranen kasar kan yakin da ake da Boko Haram.

https://p.dw.com/p/1JMMt
Protest gegen Boko Haram in Niamey, Niger
Masu zanga-zangar adawa da Boko Haram a NijarHoto: AFP/Getty Images/B. Hama

Masu zanga-zangar dai a birnin Yamai, Tahoua, da Damagaram, sun yi ta rera kalammai na nuna adawa ga Boko Haram, da kuma na goyon baya ga jami'an tsaron kasar, inda a birnin na Yamai suka yi jerin gwano kafin daga bisani su tare a harabar majalisar dokokin kasar inda suka gudanar da taron gangami.

Kungiyoyinn fararan hulla ne dai, gami da na kwadago, da kungiyoyin dalibai, suka shirya wannan zanga-zanga wadda ita ce ta biyu da aka shirya a kasar tun bayan da sojojin na Nijar suka tsunduma a cikin yaki da Boko Haram. A farkon watan Yuni ne dai da ya gabata, mayakan na Boko Haram suka hallaka sojojin na Nijar 26 tare da jikkata wasu da yawan gaske a garin Bosso da ke cikin jihar Diffa a Gabashin kasar.