1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zargin juyin mulki a kasar Malawi

March 11, 2013

Gwamnatin Malawi ta cafke wasu tsoffin ministoci bisa zargin yunkurin juyin mulki.

https://p.dw.com/p/17v09
Malawian Vice-President Joyce Banda addresses a media conference in the capital Lilongwe April 7, 2012. Banda took over the running of the southern African nation on Saturday after the death of President Bingu wa Mutharika, and fears of a succession struggle receded as state institutions backed the constitutional handover. The government only officially confirmed 78-year-old Mutharika's death earlier on Saturday, two days after he had died following a heart attack. Seated on either side of Banda are the Inspector General of Police Peter Mukhito (L) and the Army Commander General Henry Odilo. REUTERS/Mabvuto Banda (MALAWI - Tags: POLITICS MILITARY)
Hoto: Reuters

Rundunar 'yan sanda a kasar Malawi ta bayyana tsare wasu tsoffin ministocin kasar da kuma manyan jami'an gwamnati su 11 ciki kuwa harda dan uwan tsohon shugaban kasar bisa zargin yunkurin kifar da gwamnati, abinda kuma ya haddasa zanga zangar da ta sa jami'an 'yan sanda yin anfani da hayaki mai sa hawaye. Gungun mutanen dai ana zargin su ne da kokarin hana mataimakiyar shugaban kasa a wancan lokacin, wato Joyce Banda, darewa bisa kujerar shugabancin kasar a shekarar da ta gabata bayan mutuwar shugaba Bingu wa Mutharika. Daga cikin wadanda hukumomin suka tsare kuma harda Peter Mutharika, wanda ke zama ministan harkokin wajen kasar a karkashin shugabancin Bingu wa Muthawarika.

Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Mohammad Nasir Awal