1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An bindige wasu mutane takwas a Indonesiya

Gazali Abdou TasawaApril 28, 2015

Hukumomin kasar Indonesiya sun zartar da hukuncin kisa a kan wasu mutane takwas da suka samu da fataucin hodar iblis a kasar.

https://p.dw.com/p/1FGqi
Hoto: Getty Images/U. Ifansasti

An zartar da hukuncin kisan ne dai ta hanyar bindige mutanen takwas daga ciki har da 'yan Najeriya hudu da 'yan Brazil biyu da 'yan Ostreliya biyu. An bindige mutanen ne da misalin karfe biyar agogon GMT wato karfe 12 na dare kenan a kasar ta Indonesiya. Saidai an dage matakin zartar da hukuncin a wata mata 'yar kasar Philippine mai suna Marie Jean wacce itama ke cikin mutanen da aka kama da wannan laifi.