1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zimbabuwe: An jaddada bukatar cire takunkumin Turai

Zulaiha Abubakar
December 14, 2017

Sabon shugaban kasar Emmerson Mnangagwa ya yi kira ga kasashen yammacin Turai da su cire takunkumin da ke kan gwamnatinsa, a wani jawabi da ya yi wa jami'an jam'iyyar da ke mulki.

https://p.dw.com/p/2pN2J
Simbabwe neuer Präsident Mnangagwa
Hoto: Getty Images/AFP/T. Karumba

A watan da ya gabata ne dai Mnangagwa mai shekaru 75 da haihuwa ya dare kujerar jagorancin Zimbabuwe bayan da sojojin kasar da jam'iyyar ZANU-PF mai mulki suka juyawa tsohon shugaba Robert Mugabe baya, bayan shekaru 37 ya na mulki.

A shekara ta 2014 Kungiyar Tarayyar Turai ta cirewa jami'an ZANU-PF da wasu kamfanoni da sojojin kasar takunkumin tafiye tafiye, sai dai Amurka ta cigaba da nata haramcin a bangaren tattali da tafiye-tafiye a kan akasarin jami'an jam'iyyar da ke mulkin.

Kasashen duniya dai sun sa ido domin ganin yadda zabe zai gudana a shekara ta 2018 mai kamawa a Zimbabuwe, wanda shugaba Mnangagwa ya ce za'ayi shi cikin gaskiya da adalci.