1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Zimbabuwe: Shugaba Mugabe zai gana da sojoji

Gazali Abdou Tasawa
November 19, 2017

Shugaban kasar Zimbabuwe Robert Mugabe wanda da dama daga cikin magoya bayansa suka juya masa baya na shirin ganawa a wannan Lahadi da shugabannin sojojin da suke tsare da shi a gidansa tun 'yan kwanakin da suka gabata.

https://p.dw.com/p/2nscR
Simbabwe Robert Mugabe hält Rede an der Uni
Hoto: picture-alliance/dpa/AP/T. Mukwazhi

Shugaban kasar Zimbabuwe Robert Mugabe wanda da dama daga cikin magoya bayansa suka juya masa baya na shirin ganawa a wannan Lahadi da shugabannin sojojin da suke tsare da shi a gidansa, a yayin da a share daya kwamitin gudanarwa na jam'iyyarsa ta zanu PF zai gudanar da taro a wannan rana domin bayyana matsayinsa a game da makomar Shugaba Mugabe. 

Wannan na zuwa ne kwana daya bayan kasaitacciyar zanga-zangar neman shugaban ya sauka daga mulki da 'yan kasar suka shirya a biranen Harare da Bulawayo birnin na biyu mafi girma a kasar, zanga-zangar da kuma ta samu halartar 'ya'yan jam'iyyar Zanu PF ta Shugaba Mugabe da magoya bayan 'yan adawa har ma da wasu fararen fata na kasar. 

A lokacin zanga-zangar da ta gudana a jiya a birnin Harare masu zanga-zanga sun yi yinkurin yin tattaki zuwa fadar shugaban kasa, amma sojojin kasar suka taka masu birki.