1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Alakar Shugaba Muhammadu Buhari da Sanata Bukola Saraki

Uwais Abubakar Idris /LMJOctober 2, 2015

A Najeriya an kama hanyar samun kyautatuwar dangantaka tsakanin shugaban kasar Muhmmadu Buhari da shugaban majalisar dattawan kasar Bukola Saraki.

https://p.dw.com/p/1Ghm0
Hoton da ya janyo mai da martani a Najeriya
Hoton da ya janyo mai da martani a NajeriyaHoto: DW/U. Musa

A karon farko cikin watanni uku tun bayan da aka zabe shi a matsayin shugaban majalisar dattawan Najeriya an ga shugaban majalisar na raha har da dariya shi da shugaban kasar Muhammadu Buhari, yanayin da a wattani ukun da ya yi yana jagorantar majalisar bayan hasashen zaman tankiya a tsakanin bangarorin biyu ba a taba gani ba.

Rikicin Shugabanci

Yadda Sanata Bukola Saraki ya dare kan mulkin shugabancin majalisar ya haifar da zaman tankiya a tsakanin majalisar dattawan da ma samar da bangarori biyu na Unity Forum da Like minds, inda ta kai ga kama hanyar baiwa hammata iska a tsakanin bangarorin biyu, kana zaben na Saraki bai yi wa jam'iyyarsa ta APC dadi ba. Wannan sauyi dai na zama alamar da ka iya samar da mafita a kasar.

Rikicin majalisar dokokin Najeriya
Rikicin majalisar dokokin NajeriyaHoto: cc-by-sa/Shiraz Chakera

Sanin cewa a lokutan baya dai an ruwaito cewa shugaban majalisar dattawan Najeriyar ya yi iyakar kokarin ganawa da shugaban Najeriya ba tare da samun nasara hakan ba, a yanzu da aka ga wannan sauyi ko wane tasiri zai yi ga yanayin gudanar da majalisar? Alhaji Isa Tafida Mafindi gogaggen dan siyasa ne a Najeriyar ya ce hakan na da matukar muhimmanci ga dorewar siyasar kasar.

Faretin ranar 'yancin kai a Najeriya
Faretin ranar 'yancin kai a NajeriyaHoto: AFP/Getty Images/P. Utomi

Zaman tankiya a majalisun Najeriya

A majlisun dokokin da suka gabata dai zaman tankiya a tsakanin bangarori biyu na zartaswa da na majalisar dokokin Tarayyar Najeriyar ya kawo cikas ga gudanar da gwamnati musamman fanin yi wa talakawa aiki, abin da ya sanya nuna damuwa a kan halin da majalisar ta takwas ke ciki a yanzu, musamman a gwamnati APC da ita ce ta farko ta ‘yan adawa da ta kai ga madafan iko a kasar. Abin jira a ganin dai shi ne ko za'a ga canji da ma dorewar dangantakar a tsakanin sassan biyu, musamman sanin cewa shugaban majalisar dattawan na fuskantar shari'a a kotun da'ar ma'aikata bisa zargin kin bayyana kadarar da ya mallaka?