1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ƙasashen Afirka na fafutukar yaƙi da Boko Haram

Usman ShehuMay 31, 2014

Ƙasashe Maƙobtan Najeriya sun cimma yarjejeniyar murƙushe Ƙungiyar Boko Haram da sauran 'yan ta'adda a yankin.

https://p.dw.com/p/1C9ub
Ecowas Afrika Ökonomie Treffen Gipfel Abidjan Elfenbeinküste
Hoto: picture-alliance/Landov

Shugabannin ƙasashen yammacin Afirka sun yi alƙawarin haɗa hannu domin yaƙar 'yan ta'adda. Shugabannin sun sanar da haka yau Asabar a birnin Accra na ƙasar Ghana, a kwana na biyu na taron da shugaban Ghana John Dramani Mahama, wanda shi ne shugaban Ƙungiyar ECOWAS ya kira.

Taron ya tattauna hanyoyi da za a bi a yaƙi ƙungiyoyin 'yan bindiga da ke a arewacin Mali da Ƙungiyar Boko Haram a Najeriya. Shugabannin na ƙasashen na yankin yammancin Afirka da suka taru a birin Accra sun yi alƙawarin kafa wata hukumar haɗin gwiwa da za ta yi aiki a tsakiyar Afirka, domin ganin bayan 'yan ta'adda.Yanzu haka dai baya ga batun Boko Haram, akwai rikicin ƙabilanci da na addini a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, ga kuma rikicin abzinawa a arewacin Mali.

Mawallafi: Usman Shehu Usman
Edita: Abdourahamane Hassane