1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Ƙungiyar M23 ta ce za ta janye daga Goma

November 27, 2012

Amma fa bisa sharuɗan da ta gindaya wa gwamnati, na sako bursunan siyasa tare da rusa hukumar zaɓe ta ƙasar

https://p.dw.com/p/16qqa
M23 rebels patrol around Congo's Central Bank in Goma, eastern Congo, Monday Nov. 26, 2012. Regional leaders meeting in Uganda called for an end to the advance by M23 rebels toward Congo's capital, and also urged the Congolese government to sit down with rebel leaders as residents fled some towns for fear of more fighting between the rebels and army. (AP Photo/Jerome Delay)
Hoto: dapd

Ƙungiyar'yan tawaye ta M23 da ke da iko da yanki arewa maso gabashin Kwango ta ce a shirye ta ke ,ta janye da dakarunta daga garuruwan Goma da kuma Sake tare da fara yin shawarwari da shugaba Josephe Kabila amma fa bisa wasu jerin sharuɗa.

Yan tawayen sun ce tilas ne gwamantin jamhuriyar dimokaradiyyar kwango ta sako bursunan siyasar da ta ke tsare da su ,tare da rusa hukumar zaɓe ta ƙasar;to sai dai babban kwamanda dakarun kwangon Francpois Olenga ya ce suna jiran samu ummarni ne kwai domin kutsa kai cikin goma.Ya ce'' ba zamu tsaya ba abokan gaba su yi yadda suke so da mu, ya ce abin ya ishemu a kwai maciya amana da masu kawo masu dauki''.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Yahouza Sadissou Madobi