1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

A Hong Kong ana dakon tattaunawa

Yusuf BalaOctober 21, 2014

Bayan tsawon lokaci na zanga-zangar da ta durkusar da harkokin kasuwancin yankin Hong Kong, a yau Talata ana jiran ganin tattaunawa da za a yada ta kafar talibijin tsakanin gwamnati da masu fafutuka.

https://p.dw.com/p/1DZ2s
Zusammenstöße Demonstranten und Polizei Hong Kong 18.10.2014
Hoto: Alex Ogle/AFP/Getty Images

Masu fafutukar rajin kafa dimokradiya a Hong Kong sun tsaya a tituna ana kallon-kallo da jami'an 'yan sanda gabannin fara tattataunawa da bangaren gwamnati da shugabannin masu fafutukar a ranar Talatan nan.

Babu dai labarin gwabzawa tasakanin masu fafutukar da 'yan sanda a yankin kasuwancin na Mong Kok a mashigar teku ta Kowloon, daya daga cikin manyan wurare uku da wannan zanga-zanga tafi kamari.

A yammacin jiya Litinin ne babbar kotun ta Hong Kong ta bada umarni ga masu zanga-zangar da su kauracewa dandalin da suka kafa a yankin na Mong Kok.

Tattaunawar dai da aka tsara a yau Talata tsakanin masu rajin dimokradiya da bangaren gwamnati, za a yada ta ne kai tsaye ta kafar talabijin inda za a tattauna kan batun tsare-tsare na zaben kasar.