Almakura ya tsira daga zargi a Nasarawa
August 5, 2014Kwamitin da aka kafa a Jihar Nasarawa ta tarayyar Najeriya domin ya binciki zarge- zargen da ake yi wa gwamna Tanko Almakura, ya yi fatali da zarge- zarge 16 da majalisar dokokin jihar ta yi masa. A wannan Talata da rana ne a garin Lafia, shugaban kwamitin Usman Shehu, ya yanke hukuncin kan zarge- zargen bayan da kwamitin ya yi zamansa.
'Yan majalisar Nasarawa na zargin Almakura da aikata laifuka daban-daban ciki kuwa har da wawushe dukiyar talakawa. Sai dai shida ne daga cikin 'yan majalisa 20, da suka nemi tsige gwamnan suka hallara gaban kwamitin tare da lauyoyinsu, inda suka ce ba su yarda da sahihancinsa ba. Don haka ba za su bayyana ba domin amsa tambayoyin kwamitin.
Mawallafi: Abdullahi Maidawa daga Nasarawa
Edita: Mouhamadou Awal Balarabe