1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Allah ya yiwa Dan masanin Kano rasuwa

July 3, 2017

Dan Masanin Kano Alhaji Yusuf Maitama Sule ya rasu bayan gajeriyar jinya a wani asibiti a Masar.

https://p.dw.com/p/2fqhK
Nigeria neuer Emir von Kano Sanusi Lamido Sanusi
Hoto: Amino Abubakar/AFP/Getty Images

Allah ya yiwa Danmasanin Kano Alhaji Maitama Sule rasuwa.

Ya rasu a yau litinin a wani asibitin birnin Alkahira a kasar Masar inda ya je jinya.

A na sa ran dawo da gawarsa inda za'a yi masa jana'aiza a fadar mai martaba Sarkin Kano a gobe talata idan Allah ya kaimu.

Mairigayi Danmasanin Kano Alhaji maitama Sule ya rike mukamai da dama da suka hada da Jakadan Najeriya a Majalisar Dinkin Duniya da kuma ministan ma'adanai da wutar lantarki a zamanin jamhuriya ta farko. 

Ya rasu yana da shekaru 87 a duniya. Gwamnatin jihar Kano ta ware gobe Talata a matsayin ranar hutu don zaman makoki da girmamawa ga marigayin.