1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka da Turai na tir da rikicin Libiya

Usman ShehuAugust 26, 2014

Yayinda aka kasa samun dai-daito tsakanin kungiyoyin mayaka a Libiya, an yi kira da a samu sasantawa don kawo karshen zubar da jini da ke faruwa a kasar

https://p.dw.com/p/1D15B
Libyen/ Kämpfe /Tripolis
Hoto: Reuters

Kasashen Yamma na yin Allah wadai da tashin hankalin da ke faruwa a kasar Libiya. Fada tsakanin kungiyoyi da kabilu sai karuwa yake yi a kasar, tun bayan da aka kifar da gwamnatin Gaddafi a shekara ta 2011. Wata sanarwar da ta samu sa hannun kasashen Faransa, Italiya, Birtaniya, Amirka da Jamus, duk sun yi kira da a samu tsagaita wuta nan take. Sun kuma yi gargadin cewa duk wata katsalanda daga waje, zai kara dagula al'amura, kana ya kara kawo koma baya ga samar da demokradiyya a kasar ta Libiya. A jiya Litinin ne dai, 'yan majalisar dokoki suka koma aiki, inda za su rusa gwamnatin wucin gadi da aka kafa watanni biyu da suka gabata.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita: Umaru Aliyu