1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka ta damu a kan zaben Najeriya

Lateefa Mustapha Ja'afar
January 11, 2019

Kasar Amirka ta nunar da cewa babban zaben da za a gudanar a Tarayyar Najeriya cikin watan Fabarairu mai zuwa, na zaman wani zakaran gwajin dafi na dimukuradiyya a kasar.

https://p.dw.com/p/3BM8z
Nigeria wählt Gouverneure und Regionalparlamente
Shirye-shiryen babban zabe a NajeriyaHoto: Reuters/Penney

Mataimakin jakadan Amirka Jonathan Cohen ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi ga Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, inda ya nunar da cewa gwamnatin Shugaba Donald Trump na Amirkan tana da damuwa matuka kan yadda jami'an tsaron Najeriya ke cusgunawa mutane tare da shiga dumu-dumu cikin harkar siyasa. Shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari na jam'iyyar APC mai mulki dai na neman wa'adi na byiu, yayin da yake fuskantar gagarumar adawa daga dan takarar babbar jam'iyar adawar ta PDP da kuma shugabar gwagwarmayar kwato 'yan matan Chibok da kungiyar Boko Haram ta sace wato Bring Back Our Girls Oby Ezekwesili ta jam'iyyar ACPN.