1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka ta fidda matsaya tsakaninta da China

March 20, 2019

Shugaba Donald Trump na Amirka, ya ce harajin nan da kasar ta dora kan kayayyakin da China ke shigarwa Amirka, zai ci gaba har zuwa wani lokaci nan gaba.

https://p.dw.com/p/3FOCu
USA Donald Trump
Hoto: picture-alliance/Newscom/O. Douliery

Kalaman Shugaba Donald Trump na Amirka a wannan Laraba, ga dukkan alamu sun mayar da hannun agogo baya a tunanin da ake yi na cewar matsalar cinikayya tsakanin kasashen na iya sauyawa.

A makon gobe ne jami'an Amirka da na China za su gana a birnin Beijing.

Mr. Trump ya ce za su cimma yarjejeniyar cinikayyar ne kawai, muddin suka tabbatar da cewa Chinar za ta cika alkawuran da za su amince a kansu.

Amirka dai na da bukatar wasu sauye-sauye ne daga tsare-tsaren cinikayyar kasar China.