1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amirka ta kara jaddada goyon bayanta ga kasar Masar

Zulaiha Abubakar
February 12, 2018

Sakataren harkokin wajen Amirka Rex Tillerson ya jaddada aniyar kasarsa na ci gaba da ba kasar Masar cikakken goyon baya a kan yaki da ayyukan 'yan ta'adda.

https://p.dw.com/p/2sX8D
Mexiko NAFTA-Verhandlungen | Rex Tillerson
Hoto: Reuters/H. Romero

Rex Tillerson ya bayyana haka ne yayin da yake ganawa da takwaransa na kasar Masar  daga nan sai ya kara da cewar Amirka ba za ta gajiya ba wajen ganin an  gudanar da zabubbuka a kasashen Larabawa bisa cancanta,kamar yadda kasar ta dauki aniyar gani ta maido da zaman lafiya tsakanin kasashen Falasdinu da Isara'la. Duk kuwa da cewar Donald Trump ya ayyana birnin Kudus a matsayin babban birnin Isra'ila, a karshe ya roki al'ummar kasar Masar da su ci gaba da goyon bayan Amirka don maido da tsaro kasar.