1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Amnesty ta yi kiran da a janye hukuncin kisa a Edo

October 20, 2012

Hukumar kare haƙƙin bani adaman nan ta Amnesty International ta yi kira ga gwamnati jihar Edo a Najeriya da ta jingine aiwartar da kisan da za a yi wasu mutane biyu.

https://p.dw.com/p/16Til
Logo Amnesty International

Ƙungiyar dai ta ce ta yi wannan kiran ne saboda a cewarta yankewa mutanen hukuncin kisa wani babban karen tsaye ne ga 'yancinsu na mutuntaka kasancewar a halin yanzu mutanen sun ɗaukaka ƙara game da wannan hukuncin da aka yanke musu.

Da ya ke zantawa da kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP, kwamishin shari'ar jihar ta Edo Osagie Obayuwana ya ce mutanen da aka yankewa hukuncin sun ɗaukaka ƙara ne bayan lokacin da aka ɗeba musu na ɗaukaka ƙarar ya ƙare, a saboda haka yanzu kam bakin alƙalami ya bushe domin mako biyun da su ka gaba gwamnan jihar Adams Oshiomole ya sanya hannu kan takardar bada umarnin kashe mutanen.

To sai dai duk da wannan bayanai, Amnesty ɗin ta bakin muƙaddashiyar daraktan hukumar ta Afrika Lucy Freeman ta ce matakin da mahukuntan su ka ɗauka ya saɓawa 'yanci na rayuwa da kowanne bil adama ke da shi.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Zainab Mohammed Abubakar